SHUGABANCIN MACE A MUSULUNCI (IBRAHIM JALO JALINGO)
SHUGABANCIN MACE A MUSULUNCI:
1. Malaman Musulunci sun yi sabani a
kan halaccin shugabancin mace,
dalilin wannan sabani nasu kuwa shi
ne irin yadda fahimtarsu ta saba wa
juna game da wani ingantaccen
hadithin Annabi mai tsira da amincin
Allah, Hadithi na 4425 wanda Imamul
Bukhari ya ruwaito daga Sahabi Abuu
Bakrah ya ce:-
(( ﻟﻘﺪ ﻧﻔﻌﻨﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻜﻠﻤﺔ ﺳﻤﻌﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ
ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺍﻳﺎﻡ ﺍﻟﺠﻤﻞ ﺑﻌﺪ ﻣﺎ ﻛﺪﺕ
ﺍﻥ ﺍﻟﺤﻖ ﺑﺄﺻﺤﺎﺏ ﺍﻟﺠﻤﻞ ﻓﺎﻗﺎﺗﻞ ﻣﻌﻬﻢ . ﻗﺎﻝ :
ﻟﻤﺎ ﺑﻠﻎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺍﻥ
ﺃﻫﻞ ﻓﺎﺭﺱ ﻗﺪ ﻣﻠﻜﻮﺍ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺑﻨﺖ ﻛﺴﺮﻯ ﻗﺎﻝ :
ﻟﻦ ﻳﻔﻠﺢ ﻗﻮﻡ ﻭﻟﻮﺍ ﺃﻣﺮﻫﻢ ﺍﻣﺮﺃﺓ ))
Ma’ana: ((Hakika Allah Ya amfane ni
da wata kalma da na ji daga Manzon
Allah mai tsira da amincin Allah a
kwanukan Jamal bayan na yi kusa in
fada cikin sahun mutanen Jamal in yi
yaki tare da su. Ya ce: Lokacin da
labari ya riski Manzon Allah mai tsira
da amincin Allah cewa mutanen Farisa
sun nada wa kansu Yar Kisraa a
matsayin sauniyarsu sai ya ce: “Ba za
su rabauta ba mutanen da suka
jagorantar da wata mace lamarinsu)).
Masanin ilmin Hadithi Al-Haafiz Ibnu
Hajar ya ce cikin littafinsa Fathul
Baarii 7/735 a lokacin da yake yi wa
wannan Hadithi sharhi:-
(( ﻭﺍﻟﻤﻨﻊ ﻣﻦ ﺍﻥ ﺗﻠﻲ ﺍﻹﻣﺎﺭﺓ ﻭﺍﻟﻘﻀﺎﺀ ﻗﻮﻝ
ﺍﻟﺠﻤﻬﻮﺭ، ﻭﺃﺟﺎﺯﻩ ﺍﻟﻄﺒﺮﻱ، ﻭﻫﻲ ﺭﻭﺍﻳﺔ ﻋﻦ
ﻣﺎﻟﻚ، ﻭﻋﻦ ﺍﺑﻲ ﺣﻨﻴﻔﺔ ﺗﻠﻲ ﺍﻟﺤﻜﻢ ﻓﻴﻤﺎ ﺗﺠﻮﺯ
ﻓﻴﻪ ﺷﻬﺎﺩﺓ ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ )).
Ma’ana: ((Hana mace ta jibinci Mulki
da Alkalanci magana ce ta masu
rinjaye cikin Malamai. Amma
(Imaamut) Tabarii ya halatta hakan,
haka nan wata riwayar fatawa ma
daga (Imamu) Maalik. Daga Abuu
Hanifah kuwa mace tana iya yin
Alkalanci cikin mas’alolin da ake
karbar shidar mata a cikinsu)).
2. A mazhabar Hanafiyyah halal ne
mace ta yi sarutar da za a rika kiran
ta Suldan, saboda ya zo cikin babban
littafin mazhabar Hanafiyyah mai
suna Al-Bahrur Raa’q 7/5 wanda
Imam Ibnu Nujaim ya wallafa kamar
haka:-
(( ﻭﺃﻣﺎ ﺳﻠﻄﻨﺘﻬﺎ ﻓﺼﺤﻴﺤﺔ؛ ﻭﻗﺪ ﻭﻟﻲ ﻣﺼﺮ
ﺇﻣﺮﺓ ﺗﺴﻤﻰ ﺷﺠﺮﺓ ﺍﻟﺪﺭ ﺟﺎﺭﻳﺔ ﺍﻟﻤﻠﻚ ﺍﻟﺼﺎﻟﺢ
ﺑﻦ ﺃﻳﻮﺏ )).
Ma’ana: ((Amma Saldanarta (watau
mace ta yi saruatar da za a rika
kiranta Sultan) to wannan kam
ingantacce ne, saboda wata mace mai
suna Shajaratud Durr Yantacciyar
Kuyangar Sarki As-Salih Bin Ayyub ta
mulki Kasar Masar)). Watau mace ta
zamanto Shugaban Kasar Nigeria, ko
Niger, ko India, ko abin da ya yi kama
da haka wannan babu laifi a cikinsa.
Domin wannan ba’a kiransa Al-
Khilafar Kubraa.
3. Masu rinjaye cikin Malamai suna
ganin fadar Annabi mai tsira da
amincin Allah: ((Ba za su rabauta ba
mutanen da suka jagorantar da wata
mace al’amarinsu)) hakan yana nufin
Annabi ya haramta wa mace yin ko
wani mulki ne. Wannan shi ya sa suka
ce haramun ne mace ta yi shugabanci.
Sun karfafa fahimtarsu da wasu
bayanai da dama, to amma dai
ginshikin hujjarsu shi ne Hadithin Abu
Bakrah da muka ambata a sama.
4. Amma su mara sa rinjaye cikin
Malamai su ganin cewa wannan
Hadithin yana nufin mutanen Kasar
Farisa na wancan lokacin ne kadai ba
wai hukunci ba ne tabbatacce a bisa
ko wace mace cikin ko wace Al’umma
kuma a cikin ko wane zamani ba,
dalili kuwa shi ne: Su wadannan
mutane na daular Farisa da Annabi ya
yi wannan maganar a kansu hakika
ba su rabautan ba, saboda nan da nan
mulkinsu ya rushe suka koma
karkashin Daular Musulunci, amma
wannan ba ya nufin haramcin mulkin
mace, ko cewa duk inda mace ta yi
mulki to jama’ar wurin ba za su yi
nasara ba, saboda a bangarorin
Duniya da yawa Mata sun yi mulki
kuma daulolin da suka mulka ba su
rushe ba, a gaskiya ma an yi ta samun
ci gaba ne a lokacin mulkin nasu, lalle
kuwa da maganar Annabi cikin
wannan Hadithin tana nufin ko wace
Al’umma ce cikin ko wane zamani to
da kuwa dole ne dukkan inda mace ta
yi mulki daular wurin ta rushe sannan
al’ummar wurin su tabe su kasa samun
nasara cikin lamuransu, saboda
dukkan abin da Annabi mai tsira da
amincin Allah ya fada to dole he ya
faru.
5. Sannan shi wannan Hadithi da
Sahabi Abu Bakrah ya ruwaito ya
ambata shi ne domin ya ba da hujjarsa
ta rashin shiga cikin rundunar da take
karkashin Nana A’isha a yakin Jamal,
sboda a fahimtarsa hadithin yana
hana mace shugabanci, ga shi kuma a
nan Nana A’isha ce take yin
shugabancin!!
A nan ya kamata a fahimci cewa ba
dukkan Sahabbai ba ne suke da irin
wannan fahimtar ko suke kan irin
wannan mazhabar, saboda ita kanta
Nana A’isha ba ta da fahimtar cewa
cewa jagorancinta haramun ne a
Musulunci duk kuwa da yawan ilminta
da kuma yawan fiqhunta. Haka nan a
cikin wadanda suka jagorantar da ita
akwai biyu daga cikin Manyan
Sahabban da ake kira Al-Ashratul
Mubashsharuuna Bil Jannah: Az-
Zubair Bin Al-Awwam, da Talha Bin
Ubaidil Lah, wadannan manyan
Sahabbai da suna da irin wannan
fahimta ta haramta jagorancin mace
to da ba su jagorantar da Nana A’isha
a yakin Jamal ba.
6. Har yanzu Malamai masu ganin
halaccin mulkin Mace sun karfafa
wannan fahimta tasu da cewa: Idan
har a cikin Mata Musulmi wadanda
suka riski zamanin Annabi mai tsira
da amincin Allah za a sami matar da
za ta jibinci jagorancin Hisbah duk da
irin yawan wahalarsa, to kuwa mene
ne zai hana ta jibinci shugabantar
wani aiki da bai kai Hisbah wahala
ba? Suka ce: Ya zo cikin littafin
Hadithi Al-Mu’ujamul Kabiir Hadithi
na 20240 kamar haka:-
(( ﺣﺪﺛﻨﺎ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﺃﺣﻤﺪ ﺑﻦ ﺣﻨﺒﻞ، ﺣﺪﺛﻨﻲ
ﺍﺑﻲ، ﺛﻨﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﻳﺰﻳﺪ ﺍﻟﻮﺍﺳﻄﻲ، ﻋﻦ ﺍﺑﻲ
ﺑﻠﺞ ﻳﺤﻴﻰ ﺑﻦ ﺍﺑﻲ ﺳﻠﻴﻢ ﻗﺎﻝ : ﺭﺃﻳﺖ ﺳﻤﺮﺍﺀ
ﺑﻨﺖ ﻧﻬﻴﻚ ﻭﻛﺎﻧﺖ ﺃﺩﺭﻛﺖ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ : ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺩﺭﻉ ﻏﻠﻴﻆ، ﻭﺧﻤﺎﺭ ﻏﻠﻴﻆ ﺑﻴﺪﻫﺎ
ﺳﻮﻁ ﺗﻮﺩﺏ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻭﺗﺎﻣﺮ ﺑﺎﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ﻭﺗﻨﻬﻰ ﻋﻦ
ﺍﻟﻤﻨﻜﺮ )).
Ma’ana: ((Abdullahi Bin Ahmad Bin
Hanbal ya gaya mana, Mahaifina ya
gaya mini, Muhammad Bin Yaziid Al-
Waasitii ya gaya mana daga Abuu
Yahya Bin Abii Sulaiman, ya ce: Na ga
Samraa Yar Nahiik wacce ta kasance
ta yi zamani da Annabi mai tsira da
amincin Allah, na gan ta tana sanye da
wani dogon riga mai kauri, da wani
khimar mai kauri, da bulala a
hannunta tana ladabtar da mutane,
tana yin umurni da kyautayi tana yin
hani ga munkari)). Wannan Hadithi
Albaanii ya inganta shi cikin littafin
shi mai suna Ar-Raddul Mufhim shafi
na 155, da kuma littafin shi mai suna
Jilbaabul Mar’atil Muslimah shafi na
101.
7. Idan ‘yan’uwa musulmi suka
fahimci wadannan takaitattun
bayanai da muka ambata a sama, to
za su fahimci cewa ita mas’alar
shugabancin mace, watau mace ta
kasance ‘yar majalisa, ko Governor, ko
shugaban kasa, mas’ala ce ta sabanin
malamai watau mas’ala ce Khilafiyyah
da sam bai kamata a rika zurfafa
surutai a cikinta ba musamman ma a
cikin wannan zamani namu. Abin da
kawai ya kamata a yi in har an sami
irin wannan waa’qi’ah cikin
Al’ummah shi ne sai masu hankali da
basira cikin Al’ummah su dubi abin da
zai fi zama maslaha ga Al’ummar Kasa
a idanun Shari’ah.
Allah Ya taimake
mu. Ameen.
Created at 2015-11-07 11:32
Back to posts
UNDER MAINTENANCE
SHUGABANCIN MACE A MUSULUNCI (IBRAHIM JALO JALINGO) - Bloguzaifaonline.xtgem.com