FATAWOWIN MALAMAN SUNNAH GAME DA MAS'ALAR MAIDA BUDE TARO KO RUFE SHI DA YIN ADDU' A CIKIN JAMA'A WATA AL'ADAR KULLUM (IBRAHIM JALO JALINGO)FATAWOWIN MALAMAN SUNNAH GAME DA
MAS'ALAR MAIDA BUDE TARO KO RUFE SHI DA
YIN ADDU'A CIKIN JAM'I WATA AL'ADAR
KULLUM:
'Yan'uwa Musulmi! Mun rubuta a cikin takardar
seminarmu ta garin Abuju seminar da Kungiyar
Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah ta
kasa ta yi a ranakun 26-28/7/1433. 15-17/6/2012
cewa: ((Dukkan wani aikin Annabi mai tsira da
animcin Allah da ya zo bisa wata siffa, sannan
malumanmu na Sunnah suka bayyana mana
wannan siffar cikin littattafansu, to dukkan abin
da zai canja wannan siffar, ko ya bata wannan
siffar da sunan neman wata falalar Ubangiji
Madaukakin Sarki, to lalle wannan ya zama
bidi'ah cikin Addini)).
Mun bada misali da taron da Annabi mai tsira da
aminci ya sa babban Sahabi Sa'ad Dan Ubadah
ya kira, a inda shi Annabi ya halarci taron, kuma
aka yi taron har aka gama kowa ya koma inda ya
fito ba tare da yin addu'ar bude taro ko rufe shi
ba cikin jam'i kamar yadda mu muke yi kullum a
yanzu!! Mun kuma bada misalin irin yadda Umar
Dan Khattab yake yin tarurruka da gwamnoninsa
a lokacin aikin Hajji ba tare yin addu'ar bude
taro, ko addu'ar rufe taro ba.
A cikin wannan rubutu namu na yau muna so ne
mu kawo wa jama'ar musulmi masu kaunar
Sunna daga baki har zuciya fatawowin da
Malumanmu na da'awah da aqidah na duniya
suka yi game da wannan mas'alar da kuma
mas'aloli masu kama da ita. Amma kafin hakan
ga shimfida:-
NA FARKO:
Lalle, a matsayinmu na Al'ummar musulmi, ba
mu da wani abu na alheri da ya wuce yin koyi da
Annabi mai tsira da mincin Allah cikin dukkan
aqidarmu, da dukkan ibadarmu, da kuma dukkan
mu'amalarmu. Allah Madaukakin Sarki Ya ce
cikin Suratul Ahzaab Aya ta 21:-
(( ﻟﻘﺪ ﻛﺎﻥ ﻟﻜﻢ ﻓﻲ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﺳﻮﺓ ﺣﺴﻨﺔ ﻟﻤﻦ ﻛﺎﻥ
ﻳﺮﺟﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻻﺧﺮ )).
Ma'ana: ((Hakika' akwai koyi mai kyau gare ku
game da Manzon Allah ga duk Wanda ke
tsammanin Allah da kuma Ranar Lahira)). Intaha.
Sannan Annabi mai tsira da aminci ya ce cikin
hadithin Irbadh Dan Sariyah wanda Abu Dawud ya
ruwaito hadithi na 4609' da Tizrmizi hadthi na
2676' da Ibnu Majah hadithi na 42' da Ahmad
hadithi na 26,182 sannan Sheik Albani ya inganta
shi.
(( ﻓﻌﻠﻴﻜﻢ ﺑﺴﻨﺘﻲ ﻭﺳﻨﺔ ﺍﻟﺨﻠﻔﺎﺀ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻳﻦ )).
Ma'ana: ((Ina horon ku da yin riko da sunnata da
kuma sunnar Khalifofina shiryayyu..)). Intaha.
Sannan Imam Malik ya ruwaito cikin Muwattaa
atharii na 783 cewa:-
(( ﻛﺎﻥ ﻭﻫﺐ ﺑﻦ ﻛﻴﺴﺎﻥ ﻳﻘﻌﺪ ﺍﻟﻴﻨﺎ ﺛﻢ ﻻ ﻳﻘﻮﻝ ﺍﺑﺪﺍ ﺣﺘﻰ
ﻳﻘﻮﻝ ﻟﻨﺎ ﻻ ﻳﺼﻠﺢ ﺍﺧﺮ ﻫﺬﻩ ﺍﻻﻣﺔ ﺍﻻ ﻣﺎ ﺍﺻﻠﺢ ﺍﻭﻟﻪ )).
Ma'ana: ((Wahb Dan Kaisaan ya kasance yana
zama gurinmu, sannan ba ya cewa komi har sai
ya ce: Babu abin da zai gyara karshen wannan
Al'umma sai abin nan da ya gyara farkonta)).
Intaha.
NA BIYU:
Akwai wasu mutanen da saboda hamayyar da
suke yi da wasu masu wa'azi sai ka rika ganin
cewa idanunsu sun rufe ta yadda hakan zai hana
su yin aiki da ka'idodin ilmi cikin bayanan da
suke yi wa jama'a, sai ka rika ganin suna cewa:
Annabi ya ce abu kaza! Amma kuma ba za su
kawo muku nassin Annabin ba, saboda sun san
cewa karya suke yi Annabin bai fadi abin da suke
son su gaya wa mutane ya fadan ba!! Ko kuma
ka rika ganin cewa sun kafa hujja da wani hadithi
dha'ifi ba kuma tare da sun bayyana wa mutane
raunin hadithin ba!!
Lalle irin wannan tasarrufi daga masu bijire wa
gaskiya saboda kawai nuna ta'assubanci ga wani
ra'ayi, ko ga wani malami, ko ga wani bangare,
ko ga wata darika abin takaici ne matuka.
Saboda haka ina rokon Al'ummar musulmi
musamman ma mu 'yan izala da su bude
zukatansu ga maganganun maluman Sunnah da
fatawowinsu, mun sani barin mutum ga abin da
ya saba da shi abu ne mai wahalar gaske,
musamman ma in da ya dauki abin a matsayin
wata hanyar samun wata falalar Duniya ko Lahira
ne, to amma duk da haka in har bawan Allah ya
taro hankalinsa wuri guda sai ka ga karban
gaskiya ya zo masa da sauki. Allah Ya taimake
mu Ya yi mana jagora cikin dukkan lamuranmu.
Ameen.
FATAWOWIN MALAMAN DA'AWAH DA AQIDAH
Ya zo cikin littafin Fataawal Lajnatid Daa'imah
24/189-190 lambar fatawa ta: 20,451 kamar
haka:-
(( ﺱ : ﺷﺨﺺ ﻛﺎﻧﺖ ﻋﺎﺩﺗﻪ ﺍﻥ ﻳﻄﻌﻢ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﻟﻄﺎﺋﻔﺔ ﻣﻦ
ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﻛﻞ ﻳﻮﻡ ﺟﻤﻌﺔ، ﻭﺑﻌﺪ ﻗﻀﺎﺀ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﻻ
ﻳﺘﺮﻛﻮﻥ ﺃﻣﺎﻛﻨﻬﻢ ﻭﻣﺠﺎﻟﺴﻬﻢ، ﺑﻞ ﻳﻨﺘﻈﺮﻭﻥ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻷﺣﺪ
ﻣﻨﻬﻢ ﺍﻟﺬﻱ ﻋﻴﻨﻪ ﺻﺎﺣﺐ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺍﻥ ﻳﺪﻋﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻥ ﻳﺼﻞ
ﺛﻮﺍﺏ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺍﻟﻰ ﺃﻫﺎﻟﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻮﺗﻰ ﻭﺃﻗﺎﺭﺑﻬﻢ، ﻭﻓﻲ
ﺍﺛﻨﺎﺀ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻳﺮﻓﻊ ﺍﻟﺴﺎﺋﻞ ﻳﺪﻩ ﻣﻊ ﺍﻟﺤﺎﺿﺮﻳﻦ ﻭﻫﻢ
ﻳﻘﻮﻟﻮﻥ : ﺍﻣﻴﻦ . ﻓﻬﻞ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺬﻱ ﺗﺮﻓﻊ ﻓﻴﻪ ﺍﻷﻳﺪﻱ
ﺟﻤﺎﻋﺔ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺟﺎﺋﺰ ﺍﻡ ﻻ؟
ﺝ : ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺑﺎﻟﻜﻴﻔﻴﺔ ﺍﻟﻤﺬﻛﻮﺭﺓ ﻻ
ﺍﺻﻞ ﻟﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺸﺮﻉ ﺍﻟﻤﻄﻬﺮ، ﻓﺎﻟﻮﺍﺟﺐ ﺗﺮﻛﻪ؛ ﻻﻧﻪ ﺑﺪﻋﺔ
ﻭﺍﻻﻛﺘﻔﺎﺀ ﺑﻤﺎ ﺟﺎﺀﺕ ﺑﻪ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻟﺼﺎﺣﺐ
ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺑﺎﻟﺒﺮﻛﺔ ﻭﻧﺤﻮ ﺫﻟﻚ، ﻛﻞ ﺷﺨﺺ ﻳﻘﻮﻟﻪ ﺑﻤﻔﺮﺩﻩ،
ﻭﻣﻤﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻗﻮﻝ : " ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺑﺎﺭﻙ ﻟﻬﻢ ﻓﻴﻤﺎ ﺭﺯﻗﺘﻬﻢ
ﻭﺍﻏﻔﺮ ﻟﻬﻢ ﻭﺍﺭﺣﻤﻬﻢ " ﻭﻗﻮﻝ : "ﺃﻓﻄﺮ ﻋﻨﺪﻛﻢ ﺍﻟﺼﺎﺋﻤﻮﻥ
ﻭﺃﻛﻞ ﻃﻌﺎﻣﻜﻢ ﺍﻷﺑﺮﺍﺭ ﻭﺻﻠﺖ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ )).
Ma'ana: ((Tambaya: Mutum ne da al'adarsa ta
kasance ya ciyar da wasu jama'a abinci a ko
wace ranar juma'a, bayan an gama cin abincin ba
sa barin guraren zamansu, a'a su kan jira addu'a
ne daga wani cikinsu da mai abincin ya ayyana
shi domin ya roki Allah ladan abincin ya kai ga
'yan'uwansu da iyalansu mamatan, kuma a
lokacin wannan addu'ar shi mai addu'ar yana
daga hannunsa tare da mahalarta suna cewa:
amin. Ko wannan addu'ar da ake daga hannaye
cikinta a cikin jam'i bayan cin abinci halal ce, ko
kuwa a'a?
Jawabi: Aduu'ar jam'i bayan abinci a bisa
yanayin da aka ambata ba yi da asali cikin
Shari'ah Mai tsarki. Abin da ke wajibi shi ne barin
shi, saboda shi bidi'ah ce, da kuma wadatuwa da
abin da Sunnah ta zo da shi na yi wa mai abincin
addu'ar karin albarka da makamcin haka. Ko
wane mutum ya yi addu'ar shi kadan shi. Yana
daga cikin abin da ya zo cikin Sunnah, fadar: "Ya
Allah Ka yi musu albarka cikin abin da Ka azurta
su, Ka gafarta musu, Ka yi musu rahama" da
kuma fadar: "Masu azumi sun yi buda baki a
gurinku, mutanen kirki sun ci abincinku, Mala'iku
sun nema muku gafara)).
Sannan ya zo cikin littafin Mujallatul Buhuuthil
Islamiyyah 21/52 -mujallar da babban majalisar
malaman kasar Saudiyya take fitarwa- kamar
haka:-
(( ﻭﻟﻢ ﻳﺜﺒﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﻮﻻ ﺍﻭ
ﻓﻌﻼ ﺍﻭ ﺗﻘﺮﻳﺮﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﻋﻘﺐ ﺍﻟﺼﻠﻮﺍﺕ ﺍﻭ ﻗﺮﺍﺀﺓ
ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﻣﺒﺎﺷﺮﺓ ﺍﻭ ﻋﻘﺐ ﻛﻞ ﺩﺭﺱ، ﺳﻮﺍﺀ ﻛﺎﻥ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺎﺀ
ﺍﻻﻣﺎﻡ ﻭﺗﺎﻣﻴﻦ ﺍﻟﻤﺎﻣﻮﻣﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﺩﻋﺎﺋﻪ ﺍﻡ ﻛﺎﻥ ﺑﺪﻋﺎﺋﻬﻢ
ﻛﻠﻬﻢ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﻭﻟﻢ ﻳﻌﺮﻑ ﺫﻟﻚ ﺃﻳﻀﺎً ﻋﻦ ﺍﻟﺨﻠﻔﺎﺀ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻳﻦ
ﻭﺳﺎﺋﺮ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻢ، ﻓﻤﻦ ﺍﻟﺘﺰﻡ ﺑﺎﻟﺪﻋﺎﺀ
ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﻋﻘﺐ ﺍﻟﺼﻠﻮﺍﺕ ﺍﻭ ﺑﻌﺪ ﻛﻞ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﻟﻠﻘﺮﺍﻥ ﺍﻭ
ﺑﻌﺪ ﻛﻞ ﺩﺭﺱ ﻓﻘﺪ ﺍﺑﺘﺪﻉ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ )).
Ma'ana: ((Bai tabbata ba daga Annabi mai tsira
da mincin Allah ta hanyar magana, ko ta hanyar
aiki, ko ta hanyar tabbatar da abin da wani
Sahabi ya yi ko ya fada: yin addu'a cikin jam'i
bayan salloli, ko bayan karatun Kur'ani kai tsaye,
ko bayan dukkan darasi, babu wani bambanci
hakan ya kasance ne ta hanyar addu'ar liman su
kuwa mamu su rika yin amin a kan addu'arsa, ko
kuwa addu'arsu gaba daya cikin jam'i. Haka nan
ba a san hakan ba daga Khulafa'urrashiduun, da
sauran Sahabbai, Allah Ya kara musu yarda.
Saboda haka wanda ya lazimci addu'ar jam'i
bayan salloli, ko bayan ko wane karatun Kur'ani,
ko bayan ko wane darasi, to lalle wannan ya
kirkiri bidi'ah cikin Addini)). Intaha.
Sannan ya sake zuwa cikin Fataawal Lajnatid
Da'imah 28/242 lambar tambaya ta: 19,772
kamar haka:-
(( ﺱ : ﻧﺤﻦ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻮﺩﺍﻥ ﻧﺠﻠﺲ ﻓﻲ ﺣﻠﻘﺔ ﻓﻲ
ﺍﻟﻤﺴﺠﺪ ﻟﺘﻼﻭﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﺍﻟﻜﺮﻳﻢ ﻳﻮﻣﻴﺎ ﺑﻌﺪ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺠﺮ،
ﻭﻓﻲ ﻧﻬﺎﻳﺔ ﺍﻟﺘﻼﻭﺓ ﻳﺪﻋﻮ ﺭﺟﻞ ﻣﺨﺼﺺ ﻭﻳﺮﻓﻊ ﻳﺪﻳﻪ،
ﻭﻧﺤﻦ ﻧﺮﻓﻊ ﺍﻳﺪﻳﻨﺎ ﻣﻌﻪ ﻭﻧﺆﻣﻦ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ . ﻫﻞ ﻳﺠﻮﺯ ﻫﺬﺍ
ﺍﻟﻌﻤﻞ ﺍﻡ ﻻ ﻳﺠﻮﺯ؟
ﺝ : ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﺑﻌﺪ ﺍﻧﺘﻬﺎﺀ ﺍﻟﺤﻠﻘﺔ ﺍﻟﻤﺬﻛﻮﺭﺓ
ﻣﻦ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﺑﺪﻋﺔ ﻳﺠﺐ ﺗﺮﻛﻬﺎ، ﻭﻻ ﻣﺎﻧﻊ ﺍﻥ ﻛﻞ
ﺍﻧﺴﺎﻥ ﻳﺪﻋﻮ ﻟﻨﻔﺴﻪ ﻣﻨﻔﺮﺩﺍ ﺑﻌﺪ ﻓﺮﺍﻏﻪ ﻣﻦ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ
ﺍﻟﻜﺮﻳﻢ، ﺍﻭ ﻓﻲ ﻏﻴﺮ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﻮﺍﻝ؛ ﻻﻥ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻋﺒﺎﺩﺓ،
ﻭﻫﻮ ﻣﻄﻠﻮﺏ ﻛﻞ ﻭﻗﺖ ﻻ ﺳﻴﻤﺎ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻔﺮﺍﻍ ﻣﻦ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﺓ )).
Ma'ana: ((Tambaya: Mu wasu jama'a ne a Sudan,
muna zama cikin halaka a cikin masallaci saboda
karatun Kur'ani ko wace rana bayan sallar Asuba,
sannan a karshen tilawar wani mutum na
musamman zai yi addu'a ya daga hannayensa
mu ma mu daga hannayenmu tare da shi muna
yin amin a kan hakan. Ko wannan aiki yana
halatta, ko kuwa ba ya halatta?
Amsa: Wannan addu'ar jam'i bayan gama halkar
da aka ambata ta karatun Kur'ani wajibi ne a bar
shi, amma babu laifi ko wane mutum ya yi tasa
addu'ar ga kansa shi kadansa bayan gama
karatun Kur'ani Mai girma, ko ma cikin wasu
halayen koma bayan hakan, saboda Addu'ah
ibada ce, kuma ita addu'ah ana son yin ta a ko
wane lokaci, musamman ma bayan kare
Ibadah)). Intaha.
Muna fata za a dubi fatawowin nan da idanun
basira, da kuma jingine dukkan wani nau'i na
ta'assubanci.
FA'IDAH:
FATAWOWIN MALUMANMU NA DA'AWAH DA
AQIDAH NA DUNIYA
A KAN MAS'ALAR MAIDA BUDE TARO KO RUFE
SHI DA YIN ADDU'A CIKIN JAM'I WATA AL'ADA:
'Yan'uwa Musulmi! Mun rubuta a cikin takardar
seminarmu ta garin Abuju seminar da Kungiyar
Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah ta
kasa ta yi a ranakun 26-28/7/1433. 15-17/6/2012
cewa: ((Dukkan wani aikin Annabi mai tsira da
animcin Allah da ya zo bisa wata siffa, sannan
malumanmu na Sunnah suka bayyana mana
wannan siffar cikin littattafansu, to dukkan abin
da zai canja wannan siffar, ko ya bata wannan
siffar da sunan neman wata falalar Ubangiji
Madaukakin Sarki, to lalle wannan ya zama
bidi'ah cikin Addini)).
Mun bada misali da taron da Annabi mai tsira da
aminci ya sa babban Sahabi Sa'ad Dan Ubadah
ya kira, a inda shi Annabi ya halarci taron, kuma
aka yi taron har aka gama kowa ya koma inda ya
fito ba tare da yin addu'ar bude taro ko rufe shi
ba cikin jam'i kamar yadda mu muke yi kullum a
yanzu!! Mun kuma bada misalin irin yadda Umar
Dan Khattab yake yin tarurruka da gwamnoninsa
a lokacin aikin Hajji ba tare yin addu'ar bude
taro, ko addu'ar rufe taro ba.
A cikin wannan rubutu namu na yau muna so ne
mu kawo wa jama'ar musulmi masu kaunar
Sunna daga baki har zuciya fatawowin da
Malumanmu na da'awah da aqidah na duniya
suka yi game da wannan mas'alar da kuma
mas'aloli masu kama da ita. Amma kafin hakan
ga shimfida:-
NA FARKO:
Lalle, a matsayinmu na Al'ummar musulmi, ba
mu da wani abu na alheri da ya wuce yin koyi da
Annabi mai tsira da mincin Allah cikin dukkan
aqidarmu, da dukkan ibadarmu, da kuma dukkan
mu'amalarmu. Allah Madaukakin Sarki Ya ce
cikin Suratul Ahzaab Aya ta 21:-
(( ﻟﻘﺪ ﻛﺎﻥ ﻟﻜﻢ ﻓﻲ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﺳﻮﺓ ﺣﺴﻨﺔ ﻟﻤﻦ ﻛﺎﻥ
ﻳﺮﺟﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻻﺧﺮ )).
Ma'ana: ((Hakika' akwai koyi mai kyau gare ku
game da Manzon Allah ga duk Wanda ke
tsammanin Allah da kuma Ranar Lahira)). Intaha.
Sannan Annabi mai tsira da aminci ya ce cikin
hadithin Irbadh Dan Sariyah wanda Abu Dawud ya
ruwaito hadithi na 4609' da Tizrmizi hadthi na
2676' da Ibnu Majah hadithi na 42' da Ahmad
hadithi na 26,182 sannan Sheik Albani ya inganta
shi.
(( ﻓﻌﻠﻴﻜﻢ ﺑﺴﻨﺘﻲ ﻭﺳﻨﺔ ﺍﻟﺨﻠﻔﺎﺀ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻳﻦ )).
Ma'ana: ((Ina horon ku da yin riko da sunnata da
kuma sunnar Khalifofina shiryayyu..)). Intaha.
Sannan Imam Malik ya ruwaito cikin Muwattaa
atharii na 783 cewa:-
(( ﻛﺎﻥ ﻭﻫﺐ ﺑﻦ ﻛﻴﺴﺎﻥ ﻳﻘﻌﺪ ﺍﻟﻴﻨﺎ ﺛﻢ ﻻ ﻳﻘﻮﻝ ﺍﺑﺪﺍ ﺣﺘﻰ
ﻳﻘﻮﻝ ﻟﻨﺎ ﻻ ﻳﺼﻠﺢ ﺍﺧﺮ ﻫﺬﻩ ﺍﻻﻣﺔ ﺍﻻ ﻣﺎ ﺍﺻﻠﺢ ﺍﻭﻟﻪ )).
Ma'ana: ((Wahb Dan Kaisaan ya kasance yana
zama gurinmu, sannan ba ya cewa komi har sai
ya ce: Babu abin da zai gyara karshen wannan
Al'umma sai abin nan da ya gyara farkonta)).
Intaha.
NA BIYU:
Akwai wasu mutanen da saboda hamayyar da
suke yi da wasu masu wa'azi sai ka rika ganin
cewa idanunsu sun rufe ta yadda hakan zai hana
su yin aiki da ka'idodin ilmi cikin bayanan da
suke yi wa jama'a, sai ka rika ganin suna cewa:
Annabi ya ce abu kaza! Amma kuma ba za su
kawo muku nassin Annabin ba, saboda sun san
cewa karya suke yi Annabin bai fadi abin da suke
son su gaya wa mutane ya fadan ba!! Ko kuma
ka rika ganin cewa sun kafa hujja da wani hadithi
dha'ifi ba kuma tare da sun bayyana wa mutane
raunin hadithin ba!!
Lalle irin wannan tasarrufi daga masu bijire wa
gaskiya saboda kawai nuna ta'assubanci ga wani
ra'ayi, ko ga wani malami, ko ga wani bangare,
ko ga wata darika abin takaici ne matuka.
Saboda haka ina rokon Al'ummar musulmi
musamman ma mu 'yan izala da su bude
zukatansu ga maganganun maluman Sunnah da
fatawowinsu, mun sani barin mutum ga abin da
ya saba da shi abu ne mai wahalar gaske,
musamman ma in da ya dauki abin a matsayin
wata hanyar samun wata falalar Duniya ko Lahira
ne, to amma duk da haka in har bawan Allah ya
taro hankalinsa wuri guda sai ka ga karban
gaskiya ya zo masa da sauki. Allah Ya taimake
mu Ya yi mana jagora cikin dukkan lamuranmu.
Ameen.
FATAWOWIN MALAMAN DA'AWAH DA AQIDAH
Ya zo cikin littafin Fataawal Lajnatid Daa'imah
24/189-190 lambar fatawa ta: 20,451 kamar
haka:-
(( ﺱ : ﺷﺨﺺ ﻛﺎﻧﺖ ﻋﺎﺩﺗﻪ ﺍﻥ ﻳﻄﻌﻢ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﻟﻄﺎﺋﻔﺔ ﻣﻦ
ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﻛﻞ ﻳﻮﻡ ﺟﻤﻌﺔ، ﻭﺑﻌﺪ ﻗﻀﺎﺀ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﻻ
ﻳﺘﺮﻛﻮﻥ ﺃﻣﺎﻛﻨﻬﻢ ﻭﻣﺠﺎﻟﺴﻬﻢ، ﺑﻞ ﻳﻨﺘﻈﺮﻭﻥ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻷﺣﺪ
ﻣﻨﻬﻢ ﺍﻟﺬﻱ ﻋﻴﻨﻪ ﺻﺎﺣﺐ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺍﻥ ﻳﺪﻋﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻥ ﻳﺼﻞ
ﺛﻮﺍﺏ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺍﻟﻰ ﺃﻫﺎﻟﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻮﺗﻰ ﻭﺃﻗﺎﺭﺑﻬﻢ، ﻭﻓﻲ
ﺍﺛﻨﺎﺀ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻳﺮﻓﻊ ﺍﻟﺴﺎﺋﻞ ﻳﺪﻩ ﻣﻊ ﺍﻟﺤﺎﺿﺮﻳﻦ ﻭﻫﻢ
ﻳﻘﻮﻟﻮﻥ : ﺍﻣﻴﻦ . ﻓﻬﻞ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺬﻱ ﺗﺮﻓﻊ ﻓﻴﻪ ﺍﻷﻳﺪﻱ
ﺟﻤﺎﻋﺔ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺟﺎﺋﺰ ﺍﻡ ﻻ؟
ﺝ : ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺑﺎﻟﻜﻴﻔﻴﺔ ﺍﻟﻤﺬﻛﻮﺭﺓ ﻻ
ﺍﺻﻞ ﻟﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺸﺮﻉ ﺍﻟﻤﻄﻬﺮ، ﻓﺎﻟﻮﺍﺟﺐ ﺗﺮﻛﻪ؛ ﻻﻧﻪ ﺑﺪﻋﺔ
ﻭﺍﻻﻛﺘﻔﺎﺀ ﺑﻤﺎ ﺟﺎﺀﺕ ﺑﻪ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻟﺼﺎﺣﺐ
ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺑﺎﻟﺒﺮﻛﺔ ﻭﻧﺤﻮ ﺫﻟﻚ، ﻛﻞ ﺷﺨﺺ ﻳﻘﻮﻟﻪ ﺑﻤﻔﺮﺩﻩ،
ﻭﻣﻤﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻗﻮﻝ : " ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺑﺎﺭﻙ ﻟﻬﻢ ﻓﻴﻤﺎ ﺭﺯﻗﺘﻬﻢ
ﻭﺍﻏﻔﺮ ﻟﻬﻢ ﻭﺍﺭﺣﻤﻬﻢ " ﻭﻗﻮﻝ : "ﺃﻓﻄﺮ ﻋﻨﺪﻛﻢ ﺍﻟﺼﺎﺋﻤﻮﻥ
ﻭﺃﻛﻞ ﻃﻌﺎﻣﻜﻢ ﺍﻷﺑﺮﺍﺭ ﻭﺻﻠﺖ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ )).
Ma'ana: ((Tambaya: Mutum ne da al'adarsa ta
kasance ya ciyar da wasu jama'a abinci a ko
wace ranar juma'a, bayan an gama cin abincin ba
sa barin guraren zamansu, a'a su kan jira addu'a
ne daga wani cikinsu da mai abincin ya ayyana
shi domin ya roki Allah ladan abincin ya kai ga
'yan'uwansu da iyalansu mamatan, kuma a
lokacin wannan addu'ar shi mai addu'ar yana
daga hannunsa tare da mahalarta suna cewa:
amin. Ko wannan addu'ar da ake daga hannaye
cikinta a cikin jam'i bayan cin abinci halal ce, ko
kuwa a'a?
Jawabi: Aduu'ar jam'i bayan abinci a bisa
yanayin da aka ambata ba yi da asali cikin
Shari'ah Mai tsarki. Abin da ke wajibi shi ne barin
shi, saboda shi bidi'ah ce, da kuma wadatuwa da
abin da Sunnah ta zo da shi na yi wa mai abincin
addu'ar karin albarka da makamcin haka. Ko
wane mutum ya yi addu'ar shi kadan shi. Yana
daga cikin abin da ya zo cikin Sunnah, fadar: "Ya
Allah Ka yi musu albarka cikin abin da Ka azurta
su, Ka gafarta musu, Ka yi musu rahama" da
kuma fadar: "Masu azumi sun yi buda baki a
gurinku, mutanen kirki sun ci abincinku, Mala'iku
sun nema muku gafara)).
Sannan ya zo cikin littafin Mujallatul Buhuuthil
Islamiyyah 21/52 -mujallar da babban majalisar
malaman kasar Saudiyya take fitarwa- kamar
haka:-
(( ﻭﻟﻢ ﻳﺜﺒﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﻮﻻ ﺍﻭ
ﻓﻌﻼ ﺍﻭ ﺗﻘﺮﻳﺮﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﻋﻘﺐ ﺍﻟﺼﻠﻮﺍﺕ ﺍﻭ ﻗﺮﺍﺀﺓ
ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﻣﺒﺎﺷﺮﺓ ﺍﻭ ﻋﻘﺐ ﻛﻞ ﺩﺭﺱ، ﺳﻮﺍﺀ ﻛﺎﻥ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺎﺀ
ﺍﻻﻣﺎﻡ ﻭﺗﺎﻣﻴﻦ ﺍﻟﻤﺎﻣﻮﻣﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﺩﻋﺎﺋﻪ ﺍﻡ ﻛﺎﻥ ﺑﺪﻋﺎﺋﻬﻢ
ﻛﻠﻬﻢ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﻭﻟﻢ ﻳﻌﺮﻑ ﺫﻟﻚ ﺃﻳﻀﺎً ﻋﻦ ﺍﻟﺨﻠﻔﺎﺀ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻳﻦ
ﻭﺳﺎﺋﺮ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻢ، ﻓﻤﻦ ﺍﻟﺘﺰﻡ ﺑﺎﻟﺪﻋﺎﺀ
ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﻋﻘﺐ ﺍﻟﺼﻠﻮﺍﺕ ﺍﻭ ﺑﻌﺪ ﻛﻞ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﻟﻠﻘﺮﺍﻥ ﺍﻭ
ﺑﻌﺪ ﻛﻞ ﺩﺭﺱ ﻓﻘﺪ ﺍﺑﺘﺪﻉ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ )).
Ma'ana: ((Bai tabbata ba daga Annabi mai tsira
da mincin Allah ta hanyar magana, ko ta hanyar
aiki, ko ta hanyar tabbatar da abin da wani
Sahabi ya yi ko ya fada: yin addu'a cikin jam'i
bayan salloli, ko bayan karatun Kur'ani kai tsaye,
ko bayan dukkan darasi, babu wani bambanci
hakan ya kasance ne ta hanyar addu'ar liman su
kuwa mamu su rika yin amin a kan addu'arsa, ko
kuwa addu'arsu gaba daya cikin jam'i. Haka nan
ba a san hakan ba daga Khulafa'urrashiduun, da
sauran Sahabbai, Allah Ya kara musu yarda.
Saboda haka wanda ya lazimci addu'ar jam'i
bayan salloli, ko bayan ko wane karatun Kur'ani,
ko bayan ko wane darasi, to lalle wannan ya
kirkiri bidi'ah cikin Addini)). Intaha.
Sannan ya sake zuwa cikin Fataawal Lajnatid
Da'imah 28/242 lambar tambaya ta: 19,772
kamar haka:-
(( ﺱ : ﻧﺤﻦ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻮﺩﺍﻥ ﻧﺠﻠﺲ ﻓﻲ ﺣﻠﻘﺔ ﻓﻲ
ﺍﻟﻤﺴﺠﺪ ﻟﺘﻼﻭﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﺍﻟﻜﺮﻳﻢ ﻳﻮﻣﻴﺎ ﺑﻌﺪ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺠﺮ،
ﻭﻓﻲ ﻧﻬﺎﻳﺔ ﺍﻟﺘﻼﻭﺓ ﻳﺪﻋﻮ ﺭﺟﻞ ﻣﺨﺼﺺ ﻭﻳﺮﻓﻊ ﻳﺪﻳﻪ،
ﻭﻧﺤﻦ ﻧﺮﻓﻊ ﺍﻳﺪﻳﻨﺎ ﻣﻌﻪ ﻭﻧﺆﻣﻦ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ . ﻫﻞ ﻳﺠﻮﺯ ﻫﺬﺍ
ﺍﻟﻌﻤﻞ ﺍﻡ ﻻ ﻳﺠﻮﺯ؟
ﺝ : ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﻲ ﺑﻌﺪ ﺍﻧﺘﻬﺎﺀ ﺍﻟﺤﻠﻘﺔ ﺍﻟﻤﺬﻛﻮﺭﺓ
ﻣﻦ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﺑﺪﻋﺔ ﻳﺠﺐ ﺗﺮﻛﻬﺎ، ﻭﻻ ﻣﺎﻧﻊ ﺍﻥ ﻛﻞ
ﺍﻧﺴﺎﻥ ﻳﺪﻋﻮ ﻟﻨﻔﺴﻪ ﻣﻨﻔﺮﺩﺍ ﺑﻌﺪ ﻓﺮﺍﻏﻪ ﻣﻦ ﻗﺮﺍﺀﺓ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ
ﺍﻟﻜﺮﻳﻢ، ﺍﻭ ﻓﻲ ﻏﻴﺮ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﻮﺍﻝ؛ ﻻﻥ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻋﺒﺎﺩﺓ،
ﻭﻫﻮ ﻣﻄﻠﻮﺏ ﻛﻞ ﻭﻗﺖ ﻻ ﺳﻴﻤﺎ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﻔﺮﺍﻍ ﻣﻦ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﺓ )).
Ma'ana: ((Tambaya: Mu wasu jama'a ne a Sudan,
muna zama cikin halaka a cikin masallaci saboda
karatun Kur'ani ko wace rana bayan sallar Asuba,
sannan a karshen tilawar wani mutum na
musamman zai yi addu'a ya daga hannayensa
mu ma mu daga hannayenmu tare da shi muna
yin amin a kan hakan. Ko wannan aiki yana
halatta, ko kuwa ba ya halatta?
Amsa: Wannan addu'ar jam'i bayan gama halkar
da aka ambata ta karatun Kur'ani wajibi ne a bar
shi, amma babu laifi ko wane mutum ya yi tasa
addu'ar ga kansa shi kadansa bayan gama
karatun Kur'ani Mai girma, ko ma cikin wasu
halayen koma bayan hakan, saboda Addu'ah
ibada ce, kuma ita addu'ah ana son yin ta a ko
wane lokaci, musamman ma bayan kare
Ibadah)). Intaha.
Muna fata za a dubi fatawowin nan da idanun
basira, da kuma jingine dukkan wani nau'i na
ta'assubanci.
FA'IDAH:
Idan wani ya ce don me za ku hana bude tare ko
rufe taro da addu'a kullum-kullum? Alhali kuwa
Imamut Tabaraanii ya ruwaito hadithi na 3,456
cikin Almu'ujamul Kabiir daga Habiib Dan
Maslamah ya ce:-
(( ﺳﻤﻌﺖ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﻘﻮﻝ : ﻻ
ﻳﺠﺘﻤﻊ ﻣﻼ ﻓﻴﺪﻋﻮ ﺑﻌﻀﻬﻢ ﻭﻳﺆﻣﻦ ﺳﺎﺋﺮﻫﻢ ﺍﻻ ﺃﺟﺎﺑﻬﻢ
ﺍﻟﻠﻪ )).
Ma'ana: ((Na ji Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah yana cewa: Wasu mutane ba za su
hadu ba sashinsu yana addu'a sauran kuma na
cewa amiin face sai Allah Ya karba msu)).
Intaha.
Amsa a kan wannan sai a ce:
Na farko dai: wannan hadithi dha'ifi ne ba zai
yiwu a kafa hujja da shi ba. Albani ya raunana
shi cikin Silsilah Dha'ifah 12/940, da kuma cikin
Dha'ifut Targibi wat Tarhib1/70.
Na biyu kuma da ma hadithin zai inganta to da
sai a ce hadithin yana nufin guraren da Shari'ah
ta zo da yin addu'a cikin jam'i ne kawai, watau
kamar addu'ar da ake yi a cikin kuniti, ko kuwa
addu'ar da ake yi cikin sallar neman ruwan sama,
da makamcin hakan.
Allah Ka taimake mu Ka nuna mana gaskiya
gaskiya ce, Ka ba mu ikon bin ta, Ka kuma nuna
mana karya karya ce Ka ba mu ikon kin ta.
Ameen.i
UNDER MAINTENANCE