BANBANCIN FAHIMTAN MALLAMAI AKAN BUDE TARO KO RUFE TA (IBRAHIM JALO JALINGO)
A wannan darasi namu za mu magana ne a kan
kuskuren fahimtar nassin Alkur'ani Mai girma, ko
nassin hadithan manzon Allah mai tsira da
amincin Allah da wasu mutane ke yi game da
bayanan da Malaman Sunnah ke yi na hukuncin
maida bude taro ko rufe shi da addu'ah a cikin
jam'i wata sunnar da ake maimaitawa a kullum.
Ina rokon Allah da Ya buda zukatan 'yan'uwa
domin su fahimci gaskiya su karbe ta. Ameen.
***********************************
'Yan'uwa Musulmi! Abin da malaman Sunnah ke
cewa shi ne: A daina rikon bude taro ko rufe shi
da addu'a a matsayin wata Sunnar da ake
maimaitawa a kullum, ta yadda imma ba a yi
addu'ar ba sai a rika ganin an bar wata falala
mai yawa ta wuce, alhalin shi wannan lamari na
bude taro da addu'a babu inda aka ga cewa
Annabi mai tsira da amincin Allah ya yi shi koda
sau daya ne duk kuwa da cewa yana da damar
yin hakan da yin hakan wani alheri ne, ke nan
malaman Sunnah sun fahimta daga hakan cewa:
Sunnar Annabi mai tsira da amincin Allah cikin
mas'alar ita ce rashin aikata hakan, domin kamar
yadda daliban ilmi ne suka san cewa: wani lokaci
Sunnah ta kan kasance ne ta hanyar bari, wani
lokacin kuwa ta kan kasance ne ta hanyar yi.
***********************************************
Babban Malami a duniyar Sunnah Shaikhul Islam
Ibnu Taimiyah-Allah Ya yi masa rahama- ya ce
cikin littafinsa Majmuu'ul Fataawa 26/172 :-
(( ﻭﺍﻟﺘﺮﻙ ﺍﻟﺮﺍﺗﺐ ﺳﻨﺔ، ﻛﻤﺎ ﺍﻥ ﺍﻟﻔﻌﻞ ﺍﻟﺮﺍﺗﺐ ﺳﻨﺔ،
ﺑﺨﻼﻑ ﻣﺎ ﻛﺎﻥ ﺗﺮﻛﻪ ﻟﻌﺪﻡ ﻣﻘﺘﺾ، ﺍﻭ ﻓﻮﺍﺕ ﺷﺮﻁ، ﺍﻭ
ﻭﺟﻮﺩ ﻣﺎﻧﻊ، ﻭﺣﺪﺙ ﺑﻌﺪﻩ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻘﺘﻀﻴﺎﺕ ﻭﺍﻟﺸﺮﻭﻁ
ﻭﺯﻭﺍﻝ ﺍﻟﻤﺎﻧﻊ ﻣﺎ ﺩﻟﺖ ﺍﻟﺸﺮﻳﻌﺔ ﻋﻠﻰ ﻓﻌﻠﻪ ﺣﻴﻨﺌﺬ، ﻛﺠﻤﻊ
ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺼﺤﻒ، ﻭﺟﻤﻊ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﺍﻟﺘﺮﺍﻭﻳﺢ ﻋﻠﻰ
ﺍﻣﺎﻡ ﻭﺍﺣﺪ، ﻭﺗﻌﻠﻢ ﺍﻟﻌﺮﺑﻴﺔ ﻭﺃﺳﻤﺎﺀ ﺍﻟﻨﻘﻠﺔ ﻟﻠﻌﻠﻢ، ﻭﻏﻴﺮ
ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻳﺤﺘﺎﺝ ﺍﻟﻴﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ، ﺑﺤﻴﺚ ﻻ ﺗﺘﻢ ﺍﻟﻮﺍﺟﺒﺎﺕ
ﺍﻭ ﺍﻟﻤﺴﺘﺤﺒﺎﺕ ﺍﻟﺸﺮﻋﻴﺔ ﺍﻻ ﺑﻪ، ﻭﺍﻧﻤﺎ ﺗﺮﻛﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻟﻔﻮﺍﺕ ﺷﺮﻃﻪ ﺍﻭ ﻭﺟﻮﺩ ﻣﺎﻧﻊ . ﻓﺄﻣﺎ ﻣﺎ ﺗﺮﻛﻪ
ﻣﻦ ﺟﻨﺲ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﺍﺕ ﻣﻊ ﺍﻧﻪ ﻟﻮ ﻛﺎﻥ ﻣﺸﺮﻭﻋﺎ ﻟﻔﻌﻠﻪ ﺍﻭ ﺍﺫﻥ
ﻓﻴﻪ ﻭﻟﻔﻌﻠﻪ ﺍﻟﺨﻠﻔﺎﺀ ﺑﻌﺪﻩ ﻭﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ، ﻓﻴﺠﺐ ﺍﻟﻘﻄﻊ ﺑﺎﻥ
ﻓﻌﻠﻪ ﺑﺪﻋﺔ ﻭﺿﻼﻟﺔ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Dawwamanmen bari Sunnah ce, kamar
yadda dawwamanmen aiki yake Sunnah, sabanin
abin da barin shi ya kasance ne saboda rashin
bukatar yin shi, ko kuwa saboda rashin sharadin
yin shi, ko kuwa saboda samuwar abin da ya
hana yin shi, sannan bayan (mutuwar Annabi)
bukatar yin hakan ta taso, ko sharadin yin hakan
ya samu, ko abin da ke hana yin hakan ya kau,
ta yadda Shari'ah za ta nuna halaccin yin shi,
kamar hada Alkur'ani a Mus'hafi, da hada mutane
bayan limami daya a cikin sallar tarawihi, da
koyon ilmin Larabci, da haddace sunayen masu
nakalto ilmi, da wanin wannan daga cikin abin da
ake bukatarsa cikin Addini, ta yadda wajibai da
mustahabbai na Shari'ah ba sa cika sai tare da
shi, saboda da ma can (Manzon Allah) mai tsira
da amincn Allah ya bar yin shi ne saboda
kubucewar sharadinsa, ko saboda samuwar abin
da ke hana yin shi. To amma abin da (Annabi) ya
bari daga jinsin Ibadu tare da cewa da abin wani
abu ne da ya dace da Shari'ah to da ya aikata
shi, ko da ya ba da izinin a yi shi, kuma da ma
Khalifofinsa da Sahabbai sun yi shi a bayansa,
(irin wannan kam) wajibi ne a tabbatar da cewa
lalle yin shi bidi'ah ce kuma bata)). Intaha.
**************************************
Da wannan magana ta Shaikhul Islam Ibnu
Taimiyah za mu fahimci cewa: Sunnar Annabi
mai tsira da amincin Allah cikin bude taro ko rufe
taro da addu'ah ita ce: Barin yin hakan, saboda
masu yin haka suna ganin wata ibada suke yi
saboda su samu biyan bukatar Duniya da Lahira,
wannan shi ya sa ma in sun ga wasu sun yi taro
ba tare da sun yi ba sai su rika jin haushinsu, kai,
sai ma su rika zaginsu, suna ta yin musu yarfe,
da sharri, da jumhuri iri-iri!!
*************
MAIDA MARTANI GA MASU BIJIRE WA SUNNAH:
Idan wani ya kafa hujja da hadithin Abdullahi Dan
Umar wanda Tirmizi ya ruwaito cikin Sunan
hadithi na 3,502, da kuma Nasaa'i cikin Sunan
hadithi na 10,234 cewa:-
(( ﻗﻠﻤﺎ ﻛﺎﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﻘﻮﻡ ﻣﻦ
ﻣﺠﻠﺲ ﺣﺘﻰ ﻳﺪﻋﻮ ﺑﻬﺆﻻﺀ ﺍﻟﺪﻋﻮﺍﺕ ﻷﺻﺤﺎﺑﻪ : ﺍﻟﻠﻬﻢ
ﺍﻗﺴﻢ ﻟﻨﺎ ﻣﻦ ﺧﺸﻴﺘﻚ ﻣﺎ ﺗﺤﻮﻝ ﺑﻪ ﺑﻴﻨﻨﺎ ﻭﺑﻴﻦ ﻣﻌﺎﺻﻴﻚ،
ﻭﻣﻦ ﻃﺎﻋﺘﻚ ﻣﺎ ﺗﺒﻠﻐﻨﺎ ﺑﻪ ﺟﻨﺘﻚ، ﻭﻣﻦ ﺍﻟﻴﻘﻴﻦ ﻣﺎ ﺗﻬﻮﻥ
ﺑﻪ ﻣﺼﺎﺋﺐ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ، ﻭﻣﺘﻌﻨﺎ ﺑﺎﺳﻤﺎﻋﻨﺎ ﻭﺍﺑﺼﺎﺭﻧﺎ ﻭﻗﻮﺗﻨﺎ ﻣﺎ
ﺍﺣﻴﻴﺘﻨﺎ، ﻭﺍﺟﻌﻠﻪ ﺍﻟﻮﺍﺭﺙ ﻣﻨﺎ، ﻭﺍﺟﻌﻞ ﺛﺎﺭﻧﺎ ﻋﻠﻰ ﻣﻦ
ﻇﻠﻤﻨﺎ، ﻭﺍﻧﺼﺮﻧﺎ ﻋﻠﻰ ﻣﻦ ﻋﺎﺩﺍﻧﺎ، ﻭﻻ ﺗﺠﻌﻞ ﻣﺼﻴﺒﺘﻨﺎ ﻓﻲ
ﺩﻳﻨﻨﺎ، ﻭﻻ ﺗﺠﻌﻞ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ ﺍﻛﺒﺮ ﻫﻤﻨﺎ ﻭﻻ ﻣﺒﻠﻎ ﻋﻠﻤﻨﺎ، ﻭﻻ
ﺗﺴﻠﻂ ﻋﻠﻴﻨﺎ ﻣﻦ ﻻ ﻳﺮﺣﻤﻨﺎ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Kadan ne za a ce Mnazon Allah mai
tsira da amincin Allah ya tashi daga wata
majalisa ba tare da ya yi wa Sahabbansa addu'a
da wadannan addu'o'i ba: Ya Allah Ka ba mu
wani abu na tsoronKa da zai shiga tsakaninmu da
sabonKa, da wani abu na da'arKa da zai kai mu
aljannarKa, da wani abu na yakini da zai kai
saukaka mana musibun Duniya, ka jiyarda mu
dadi da jinmu, da ganinmu, da karfinmu matukar
dai Ka rayar da mu, Ka zamar da shi mai gado
gare mu, Ka sanya ramuwar gayyarmu a kan
wanda ya zalunce mu, Ka taimake mu a kan
wanda ya nuna mana kiyayya, kada Ka sanya
musibarmu a cikin addininmu, kada Ka sanya
Duniya mafi girman hamminmu, ko iya matukar
ilminmu, kada Ka dora wanda ba ya tausaya
mana a kanmu)). Intaha.
Idan wani ya kafa hujja da wannan hadithin to
sai a ce da shi: Shi wannan hadithin abin da
kawai ya ce shi ne: "Yan lokuta kadan ne za ce
Annabi ya tashi daga wata majalisa ba tare da ya
yi wa sahabbansa addu'a ba" hadithin bai ce
Annabi yana ce wa sahabbansa ne: ku yi salati
goma-goma sannan ya rika yin addu'a su kuma
suna cewa: ameen ba!!! Babu wani magabaci da
ya yi wa hadithin wannan fahimta, babu kuma
wani malami daga cikin masu yi wa hadithai
sharhi -a iya sanina- da ya yi wa hadithin wannan
fahimta, babu daya daga cikin maluman Da'awah
da Aqidah da ya yi wa hadithin wannan fahimta!!!
Sannan ko shakka babu da da wannan surar ce
Annabi yake yin addu'ar to da an nakalto mana
ita, saboda sura ce mai jan hankulan mutane
sosai, domin kowa ya kan bar abin da yake yi ne
domin ya saurari mai yin addu'a bayan ya yi
salati sannan kuma ya rika fadar ameen.
Sannan a cikin hadithin an ce:-
(( ﻣﻦ ﻣﺠﻠﺲ ))
Watau: daga ma ko wace majlisa. Ke nan
wannan ya hada da majalisar tattauna lamuran
duniya na yau da gobe, da majalisar wani darasi,
da majalisar koma mene ne. In da kuwa lalle
yana yin addu'ar ne a bisa surar da muke yi, to
da kuwa an nakalto mana ita. Sannan kuma da
Malumanmu na Da'awah da Aqidah ba su hana
yin addu'a cikin irin ita wannan surar ba a farko
ko karshen majalisar wani darasi, ko majalisar
karatun Kur'ani ba, da sauransu.
Sannan abu na biyu shi ne: Mene ne ya hada
tsakanin cewa Annabi yana yi wa Sahabbansa
addu'a cikin mafi yawan majalisu, da kuma cewa
Annabi yana addu'ar bude taro da rufe taro cikin
jam'i, in ba ta'assubanci da son zuciya ba? Ga
misali: Abu Dawuda ya ruwaito hadithi na 3,203,
da Tirmizi hadithi na 1,024, da Nasa'ii hadithi na
1,986' da Ibnu Majah hadithi na 1,498, da Ahmad
hadithi na 17,581 daga Sahabi Abu Hurairah da
waninsa cewa Annabi mai tsira da amincin Allah
ya kasance yana yi wa Sahabbai rayayyu da
matattu maza da mata manya da yara addu'a
cikin sallar janaza. Ga ma yadda nassin yake:-
(( ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﺤﻴﻨﺎ ﻭﻣﻴﺘﻨﺎ ﻭﺻﻐﻴﺮﻧﺎ ﻭﻛﺒﻴﺮﻧﺎ ﻭﺫﻛﺮﻧﺎ
ﻭﺍﻧﺜﺎﻧﺎ ﻭﺷﺎﻫﺪﻧﺎ ﻭﻏﺎﺋﺒﻨﺎ . ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻣﻦ ﺍﺣﻴﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺎﺣﻴﻪ
ﻋﻠﻰ ﺍﻻﻳﻤﺎﻥ ﻭﻣﻦ ﺗﻮﻓﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺘﻮﻓﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻻﺳﻼﻡ . ﺍﻟﻠﻬﻢ
ﻻ ﺗﺤﺮﻣﻨﺎ ﺍﺟﺮﻩ ﻭﻻ ﺗﻀﻠﻨﺎ ﺑﻌﺪﻩ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Ya Allah Ka gafarta wa rayayyunmu da
matattunmu, da kanananmu da manyanmu, da
mazanmu da matanmu, da halartattunmu da
wadanda ba sa nan daga cikinmu. Ya Allah
wanda Ka raya shi daga cikinmu to Ka raya shi a
kan Imani, Wanda kuma Ka matar daga cikinmu
to Ka matar da shi a kan Musulunci. Ya Allah
kada Ka haramta mana ladansa, kada kuma Ka
batar da mu bayansa)). Intaha.
A nan addu'a ce da Annabi yake yi wa
Sahabbansa, rayayyu da matattu, amma kuma shi
kadai yake yin ta ba ma dole ba ne jama'ar da ke
tare da shi su abin da yake fada, kuma babu
salatin Annabi goma-goma a cikinta, babu kuma
fadar ameen daga sauran jama'a. Lalle yadda ita
wannan addu'ar take to haka ma addu'ar:-
(( ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻗﺴﻢ ﻟﻨﺎ ﻣﻦ ﺧﺸﻴﺘﻚ ﻣﺎ ﺗﺤﻮﻝ ﺑﻪ ﺑﻴﻨﻨﺎ ﻭﺑﻴﻦ
ﻣﻌﺎﺻﻴﻚ ......)).
take, wannan shi ya sa ma su wadannan
kalmomi ba sa canja wa, kamar yadda wadancan
su ma ba sa canjawa.
Sannan abu na biyu shi ne: Akwai gurare da
yawa da Annabi mai tsira da amincin Allah yake
yi wa Sahabbai addu'a, to amma maluman
Sunnah ba su fahimci cewa addu'ar jam'i ne
yake yi ba. Misali:-
1-Hadithi na 5108 da Abu Dawud ya ruwaito, na
4623 da Abu Ya'ala ya ruwaito cikin Musnad, na
140 da Ibnul Jaaruud ya ruwaiton cikin Muntaqa
daga A'isha Allah Ya kara mata yarda ta ce:-
(( ﻛﺎﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﺆﺗﻰ ﺑﺎﻟﺼﺒﻴﺎﻥ
ﻓﻴﺪﻋﻮ ﻟﻬﻢ ﺑﺎﻟﺒﺮﻛﺔ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Manzon Allah mai tsira da amincin
Allah ya kasance ana zuwa masa da yara yana
musu addu'ar samun albarka)). Intaha. Wannan
hadithin Albanii ya inganta shi cikin Alkalimut
Tayyib 1/162. Lalle a nan hadthin ba ya nufin
jam'in addu'a Annabi yake yi watau ya umurci
mutane su daga hannu suna cewa Ameen shi
kuwa yana Ddu'a.
2-Hadithi na 502 da Bukharii ya ruwaito cikin
Al'adabul Mufrad, da hadithi na 9969 da Baihaqii
ya ruwaito cikin Shu'abul Iman cewa:-
(( ﺟﺎﺀﺕ ﺍﻟﺤﻤﻰ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻓﻘﺎﻟﺖ :
ﺍﺑﻌﺜﻨﻲ ﺍﻟﻰ ﺍﺛﺮ ﺍﻫﻠﻚ ﻋﻨﺪﻙ . ﻓﺒﻌﺜﻬﺎ ﺍﻟﻰ ﺍﻷﻧﺼﺎﺭ ﻓﺒﻘﻴﺖ
ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺳﺘﺔ ﺍﻳﺎﻡ ﻭﻟﻴﺎﻟﻴﻬﻦ ﻓﺎﺷﺘﺪ ﺫﻟﻚ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﻓﺎﺗﺎﻫﻢ ﻓﻲ
ﺩﻳﺎﺭﻫﻢ ﻓﺸﻜﻮﺍ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻪ، ﻓﺠﻌﻞ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﻳﺪﺧﻞ ﺩﺍﺭﺍ ﺩﺍﺭﺍ ﻭﺑﻴﺘﺎ ﺑﻴﺘﺎ ﻳﺪﻋﻮ ﻟﻬﻢ ﺑﺎﻟﻌﺎﻓﻴﺔ .((
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Zazzabi ya zo gurin Annabi mai tsira
da amincin Allah sai ya ce: aika ni zuwa ga
mutanen da suka fi soyuwa gare ka. Sai ya aika
da shi zuwa ga Ansarawa, ya je ya zauna a
cikinsu yini shida da dare shida, hakan ya
tsananta a kansu, sai ya je musu cikin
unguwarsu, sai suka yi masa kukan wannan
zazzabin. Sai Annabi mai tsira da amincin Allah
ya rika shiga bangare bangare, gida gida yana
musu addu'ar samun lafiya)). Intaha. Wannan
hadithin Albaanii ya inganta shi cikin Silsilah
Sahihah lamba na: 2502. A nan ma babu wani
mai sharhin hadithai da ya ce addu'ar jam'i aka
yi Annabi na addu'a saura jama'a na cewa:
ameen.
3-Hadithi na 1668 da Malik ya ruwaito cikin
Muwattaa, da hadithi na 17,959 da Tabaraanii ya
ruwaito cikin Almu'ujamul Kabir, da hadithi na
9,503 da Abdur Razzaq ya ruwaito cikin
Musannaf daga Abu Burdah cewa:-
(( ﺍﻥ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﻮﻡ ﺣﻨﻴﻦ ﺃﺗﻰ ﺍﻟﻘﺒﺎﺋﻞ
ﻳﺪﻋﻮ ﻟﻬﻢ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Annabi mai tsira da amincin Allah ya je
wa Kabilu a ranar yakin Hunain yana musu
addu'a)). Intaha. Mai littafin Majma'uz Zawaa'id
5/407 ya ce: Mazajen isnadin Mazajen Buharii da
Muslim ne, in banda Abdullahi Ibnul Mugiirah shi
kuwa thiqah ne. A nan ma babu wanda ya ce
Annabi ya je yana addu'ar ne sannan ya umurci
Kabilun da su rika cewa: ameen.
4- Hadithi na 4,546 da Haakim ya ruwaito cikin
Mustadrak daga Waliid Dan Uqbah cewa:-
(( ﻟﻤﺎ ﻓﺘﺢ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻣﻜﺔ ﺟﻌﻞ
ﺍﻫﻞ ﻣﻜﺔ ﻳﺄﺗﻮﻥ ﺑﺼﺒﻴﺎﻧﻬﻢ ﻓﻴﻤﺴﺢ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺭﺅﻭﺳﻬﻢ ﻭﻳﺪﻋﻮ ﻟﻬﻢ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Lokacin da Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah ya bude Makka, mutanen Makka
sun yi ta kawo yaransu Manzon Allah yana ta
shafan kawunansu yana musu addu'a)). Intaha. A
nan ma babu wani mai sharhin hadithi da ya ce:
Annabi ya ce su yi ta cewa ameen ne a lokacin
da yake yi wa yaran nasu addu'a. watau babu
wanda ya ce addu'ar jam'i Annabi ya yi.
****************************************
AMSA A KAN WATA MAGANAR KUMA:
Idan wani ya kafa hujja da wadannan Nassosi
kamar:-
(( ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺟﺎﺀﻭﺍ ﻣﻦ ﺑﻌﺪﻫﻢ ﻳﻘﻮﻟﻮﻥ ﺭﺑﻨﺎ ﺃﻏﻔﺮﻟﻨﺎ
ﻭﻻﺧﻮﺍﻧﻨﺎ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺳﺒﻘﻮﻧﺎ ﺑﺎﻹﻳﻤﺎﻥ .(( ﺍﻟﺤﺸﺮ :١٠ .
Ma'ana: ((Wadanda suka zo daga bayansu suna
cewa: Ya Ubangijinmu! Ka gafarta mana, da
kuma 'yan'uwanmu wadanda suka riga mu yin
Imani)). Intaha. Da kuma:-
(( ﻗﻞ ﻣﺎ ﻳﻌﺒﺆ ﺑﻜﻢ ﺭﺑﻲ ﻟﻮﻻ ﺩﻋﺎﺅﻛﻢ .(( ﺍﻟﻔﺮﻗﺎﻥ : ٧٧ .
Ma'ana: ((Ka ce: Ubangijina ba ya kulawa da ku,
in ba domin addu'arku ba)). Intaha. Da kuma:-
(( ﻭﺍﺫﺍ ﺳﺎﻟﻚ ﻋﺒﺎﺩﻱ ﻋﻨﻲ ﻓﺎﻧﻲ ﻗﺮﻳﺐ ﺃﺟﻴﺐ ﺩﻋﻮﺓ
ﺍﻟﺪﺍﻉ ﺍﺫﺍ ﺩﻋﺎﻥ .(( ﺍﻟﺒﻘﺮﺓ : ١٨٦ .
Ma'ana: ((Idan bayiNa suka tambaye ka labariNa
to Ni kusa Nake, kuma ina amsa addu'ar mai
addu'a in ya kira Ni)). Intaha. Da kuma sauran
Nassosi masu kama da haka ya ce kuma: Lalle
mu muna hana a yi sa Musulmi addu'a ne, alhalin
Allah Ya ce a roke Shi zai kuma amsa!!!
Farko dai sai a ce da su tarihi ne yake maimaita
kan sa, tsakanin maluman Sunnah da kuma masu
bidi'a da bautar son zuciya. Misali: lokacin da
Shehu Uthmanu Dan Fodiyo ya ce cikin littafin
shi Ihya'us Sunnah shafi na 102:-
(( ﻭﻣﻦ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﺩﺑﺮ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﺑﻜﻴﻔﻴﺔ ﻣﻌﻠﻮﻣﺔ ﻭﻫﻮ ﺍﻥ
ﻳﺪﻋﻮ ﺍﻻﻣﺎﻡ ﻭﻳﺆﻣﻦ ﺍﻟﻨﺎﺱ، ﻭﻫﻮ ﺑﺪﻋﺔ ﻣﻜﺮﻭﻫﺔ ﻓﻲ
ﻣﺬﻫﺐ ﻣﺎﻟﻚ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Daga cikin wannan akwai addu'a bayan
Salla a bisa wani yanayi sananne, shi ne kuwa:
Liman yana addu'a Mamu suna cewa ameen. Shi
wannan bidi'a ce makruuhiya a cikin mazhabar
Imam Malik)). Intaha. A lokacin da Shehu Dan
Fodiyo da kuma ire-irensa suka fadi haka saboda
neman jama'a su yi Musuluncisu kamar yadda
Annabi da Sahabbai suka yi an samu wasu masu
ta'assubanci wadanda kiyayya da hasada suka
cika zukatansu, da suka ki yin aiki da wannan
bayani na ilmi da so wa Musulmi alheri, suka
koma suna ta kafa hujja da irin wadannan dalilai
aammah, wadanda masu ilmi sun san cewa ba za
nuni a kan bigiren da aka yi sabani a kan shi.
Kamar dai mutumin da za ka ce da shi: ka daina
yin Salatul fatih ka rika yin Salatin da Annabi mai
tsira da amincin Allah ya koya wa Sahabbai.
Sannan shi kuma ya rika gaya wa jama'a cewa:
Kai din nan ka hana a rika yi wa Annabi salati!!!
Ko kuma ka ce a daina zikirin bidi'ah na ihu da
bugun kirji, ko bisa wani adadi wanda ba Shari'a
ce ta bayyana ba. Sai kuma a ce: Kai din nan
wai ka hana a yi wa Allah zikiri duk kuwa da
cewa Nasosi da yawa sun yi umurni da yin
hakan!!
Na biyu sai a ce da su: Irin wannan tuhumar ba
sabon lamari ba ne ga Maluma masu da'awah
wadanda suke kokarin maida mutane a kan
Sunnar Annabi mai tsira da amincin Allah cikin
dukkan lamuransu. Imam Abdur Razzaq ya
ruwaito cikin littafinsa Musannaf atharii na 4,755
da kuma Imamul Baihaqii a cikin Assunanul
Kubra atharii na 4,621 daga Sa'id Dan Musayyib
cewa:-
(( ﺍﻧﻪ ﺭﺃﻯ ﺭﺟﻼ ﻳﺼﻠﻲ ﺑﻌﺪ ﻃﻠﻮﻉ ﺍﻟﻔﺠﺮ ﺍﻛﺜﺮ ﻣﻦ
ﺭﻛﻌﺘﻴﻦ ﻳﻜﺜﺮ ﻓﻴﻬﺎ ﺍﻟﺮﻛﻮﻉ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ، ﻓﻨﻬﺎﻩ، ﻓﻘﺎﻝ : ﻳﺎ
ﻣﺤﻤﺪ ! ﻳﻌﺬﺑﻨﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺼﻼﺓ؟ ﻗﺎﻝ : ﻻ ﻭﻟﻜﻦ ﻳﻌﺬﺑﻚ
ﻋﻠﻰ ﺧﻼﻑ ﺍﻟﺴﻨﺔ .(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Ya ga wani mutum yana salla fiye da
raka'a biyu bayan fitowar alfijir yana yawaita
ruku'i da sujjada cikin sallar, sai ya hana shi. Sai
mutumin ya ce: Ya Abu Muhammad! Yanzu a kan
salla ne Allah zai azabtar da ni? Sai ya ce: A'a
zai azabtar da kai ne a kan sabawa Sunnah)).
Intaha. Sheik Albani bayan ya kawo wannan
magana cikin littafinsa Irwa'ul Galil 2/236 kuma
ya inganta isnadinta sai ya ce:-
(( ﻭﻫﺬﺍ ﻣﻦ ﺑﺪﺍﺋﻊ ﺃﺟﻮﺑﺔ ﺳﻌﻴﺪ ﺑﻦ ﺍﻟﻤﺴﻴﺐ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ
ﺗﻌﺎﻟﻰ، ﻭﻫﻮ ﺳﻼﺡ ﻗﻮﻱ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﺒﺘﺪﻋﺔ ﺍﻟﺬﻳﻦ
ﻳﺴﺘﺤﺴﻨﻮﻥ ﻛﺜﻴﺮﺍ ﻣﻦ ﺍﻟﺒﺪﻉ ﺑﺎﺳﻢ ﺍﻧﻬﺎ ﺫﻛﺮ ﻭﺻﻼﺓ، ﺛﻢ
ﻳﻨﻜﺮﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻧﻜﺎﺭ ﺫﻟﻚ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﻳﺘﻬﻤﻮﻧﻬﻢ
ﺑﺎﻧﻬﻢ ﻳﻨﻜﺮﻭﻥ ﺍﻟﺬﻛﺮ ﻭﺍﻟﺼﻼﺓ !! ﻭﻫﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻘﻴﻘﺔ ﺍﻧﻤﺎ
ﻳﻨﻜﺮﻭﻥ ﺧﻼﻓﻬﻢ ﻟﻠﺴﻨﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺬﻛﺮ ﻭﺍﻟﺼﻼﺓ ﻭﻧﺤﻮ ﺫﻟﻚ .((
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma'ana: ((Wannan yana daga cikin kyawawan
jawaban Sa'idu Dan Musayyib Allah Madaukakin
Sarki Ya yi masa rahama, sannan kuma shi
makami ne mai karfi a kan 'yan bidi'a da suke
ganin kyawun da yawa daga cikin bidi'o'i da
sunan cewa: Ai zikiri ne, da Salla! Sannan kuma
su yi wa Ahlus Sunnah inkarin inkarin da suke yi
musu, kuma su tuhumce su da cewa: Suna hana
zikirin Allah da kuma Salla!! Wanda kuma a
gaskiyar al'amari su suna musu inkarin barin
Sunnah ne da suka yi cikin Zikirin da kuma Sallar,
da abin da ya yi kama da haka)). Intaha.
Muna rokon Allah Madaukakin Sarki ya nuna
mana gaskiya gaskiya ce ya kuma ba mu ikon
aiki da ita. Ya kuma nuna mana karya karya ce
ya ba mu ikon guje mata. Ameen.
Created at 2015-12-04 20:43
Back to posts
UNDER MAINTENANCE